ZAKKATUL FITR




Zakkar Fidda kai (Zakkatul Fitr), sadaka ce da aka farlanta domin tsarkake mai azumi daga kurakurai da yi a cikin watan Ramadhan, tare da nuna godiya ga Allah, zumunci da kyautayi tsakanin musulmi.


Tana wajaba ne a kan iya mutumin da yake da abincin da ya fi Æ™arfin cikinsa (mawadaci). Zai kuma fiddawa duk wanda yake Æ™arÆ™ashin ciyarwasa (mis. ‘ya’ya, mata, iyaye, yaran gida dss). Matashi mai ciyar da kansa kuma, zai fiddawa iya kansa ne kawai. 


Ana fitar da SA’I (mudu 4/2.15kg) na abinci da mutanen gari suka fi ci (mis. Masara, shinkafa, alkama, gero/dawa dss a nan). Kamar yadda a lokacin Annabi mutanen yanki sahara suna amfani da sha’ir, dabino, alkama. 


Ana iya fitar da ita da sauran kwana biyu, ko ɗaya kafin Idi, ko a safiyar Idi kafin a yi sallar idi (Ibn Umar: Abu Dawood, 1609). Ana kuma bawa rukunin mutane takwas (8) da addinin ya ce a bawa Zakka (Tauba, 60). An hikimta hakan ne domin tausasa zuciyar marasa ƙarfi, tare da wadata su da abinci a ranar Idi.


Saboda lalurorin rayuwa da kuma ci gaban zamani, Malamai sun bada fatawar za a bayar da kuɗi madadin abinci, in an kiyasta. Wannan shi ne a taƙaice, Allah shi ne mafi sani.


Allah ya karÉ“a mana ibadu da addu’o’inmu, amin. Fatan an sha ruwa lafiya. 


© Aliyu M. Ahmad

28091441AH 21052020CE

Post a Comment

0 Comments