SHARIA BA ZATA SAƁAWA HANKALI BA; SABODA HANKALI SHI NE SHARIA



HANKALI DA ADDINI (MUSULUNCI)

Hankali (mind/العقل); shi ne dama Ubangiji (Allah) ya yiwa ɗan Adam na tantance abun da suke daidai/dace da wanin haka (rashin hankali/hauka) ta hanyar ilimi (epistemic), tunani (thinking/التفكر), bincike (researching/البحث) da bibiyar al’amura daban-daban da suka shafi rayuwarsa ta yau da kullum, kama daga addini, mu’amala da nazari cikin halittu domin tabbatar da wani abu, ko kore shakku.


Wannan dalili yasa babu wani addini (Musulunci ko waninsa), ko tsarin mulki (أحكام السلطانية) ko ƙasa (ta Musulunci, ko ta Musulmai ko Secular) da suka bawa wani abu muhimmanci fiye da hankali. Duba da ɗorawa mabiyin addinin wani nauyi (تخليف) na wata bauta (ie. Sallah, Azumi, Aikin Hajji dss), jagoranci al’umma (shugabanci), shiga mu’amala (kasuwanci, yarjejjeniya, wakilci). Saboda hadisi Shugaba (S.A.W.):

رفع القلم عن الثلاث: الصبي حتى يبلغ، والمجنون حتى يفيق ، والنائم حتى يستقيظ
]الترمذي، النسائي وإبن ماجه[

Wannan zai nuna maka muhimmancin da addini (Musulunci) ya bawa hankali; shi yasa babu wani nauyi da addini (Musulunci) ke ɗorawa kan wanda babu hankali a tare da shi (e.g. yaro, mahauci da mai bacci), domin sai da hankali mutum zai fahimci Sharia.

Haka nan, babu wani abu da dokar addini ko ƙasa take karewa da martabawa fiye hankali, idan har kayi duba na-nutsuwa cikin kowannen tsarin doka walau dinan ko zamanan zaka tarar tana da alaƙa da bawa hankali kariya; misali haramta shan kayan maye (Intoxication/السخرية) (Ma’ida: 90-91), haramta duk wani abu da zai tadawa ɗan Adam hankali ko takurawa tunaninsa (nuisance/إزعاج) (Shura:42), haramta duk wani abu da ya saɓa da al’adar hankali (bokanci, sihiri/witchcraft/السحر) (Baqara:102), tsoratarwa (intimidation/التخويف), fushi (Anger/غضد) dss.

Sannan idan ka ji an kawo wata aya a cikin Alkur’ani Maigirma, wacce take ɗauke da wani babban muhimmin saƙo ko nuna aya cikin manya ayoyin/halittun Allah sai kaji an ce maka WANNAN AYACE GA MASU HANKALI; misali: Baqara: 164, Aal-Imran: 190, Yusuf: 111, Ar-Rad: 19,Ibrahim: 52, Hajj: 46, Yasin: 62, Sad; 29, Zumar: 9 & 21, Jathiya: 5, Hadid, 17 dss.


Cikin ni’imar Allah, Allah Ya banbanta ɗan Adam da wasu halittu (dabbobi) da matakin hankali (mind/العقل) da tunani (thinking/التفكر). Wanda da ba don hankali ba, da mu mutane (Ƴan Adam) da dabobbin duk ɗaya muke babu banbanci, saboda akuya ma tasan idan tana jin yunwa ta ci abinci, idan ta fita daga gida tasan hanyar dawowa, ta san uwarta da danginta, kai har in ka dake tama ta kan jin zafi, idan ta ji matsuwa (fitsari ko bayan gari) ta ɗan sukunya ta yi, idan ta ji sauti na tsoro ko ta ga wani abu mai cutarwa (kamar kura) zata razana ta gudu, idan ta ji ƙamshin dusa ko ciyawa takan shaawi ta ci, har idan shaawarta ta tashi (sexual desire/craving) takan nemi a biya mata buƙatarta.

A ƙoƙarin Addinin Musulunci na kare martabar hankalin dan Adam; An ruwaito hadisi daga Nana A’isha (R.); Ta ji Shugaba (S.A.W.) Yace:

"إذا وضع العشاء وأقيمت الصلاة فابدءوا بالعشاء"

Ba wai don cin-abinci ya fi Sallah muhimmanci ba ne, a’a sai don kar ka je Sallah hankalinka ya rabu biyune. A wata  ruwayar ma ta Hassan ibn Ali ibn Abi Talib (R.), idan har mutum na da kokwanto cikin wani abu, to ya koma ya kama abin da babu kokwanto a ciki: Shugaba (S.A.W.) Yace:

"دع ما يريبك إلى ما لا يريبك"


Sannan yadda Ubangiji (SWT) ya kaddara aikin harshe jin ɗanɗano (taste/الطعم), idanu kallo (sight/البصر), kunne jin sauti (hearing/السمع), sai ya halittan mana zuciya da kwakwalwa domin mu riƙa tunani (thinking/التفكر) da nazari/tadabburi da hankalin da ya bamu, ya kuma sanya mana ambatonsa (الذكر) abinci ga zukatanmu domin kwantarwa da ruhi hankali da samun nutsuwa (الطمانينة) (Raad:28).

Na san wani zai iya tambayar kansa; shin ko menene fa’idar wannan rubutu mai yawan maimaituwar wannan kalmaHANKALI’?


Don ka cirewa zuciyarka cewa babu wani abu da Addinin Musulunci zai kawo maka na tsare-tsarensa (Sharia) kace wai SHARIA TA SABAWA HANKALI, sai dai kace ILIMI SABANIN JAHILCI (shawara kurum kayi karatu).


خير الكلام من قل ودل. سبحانك اللهم وبحمدك، أشهد أن لا إله إلا أنت أستغفرك وأتوب إليك.


28th Dhul-Qa’adah, 1438AH

(Sun. 20th August, 2017CE)

Post a Comment

1 Comments

  1. Muna fa'idan tuwa da rubututtukan ka Allah ya saka da alkhairi

    ReplyDelete